:
Breaking News

N E N HAUSA

Amnesty International Ta Nuna Damuwa Kan Tsare Matashin Borno, Samaila Ibrahim Kaigama

Amnesty International Ta Nuna Damuwa Kan Tsare Matashin Borno, Samaila Ibrahim Kaigama

NBA Ta Yi Allah-Wadai da Sace Alkalin Babbar Kotun Kebbi, Ta Bukaci a Gaggauta Ceto Shi

Kungiyar Lauyoyin Nijeriya (Nigerian Bar Association – NBA) ta yi kakkausar suka kan sace Mai Shari'a Faruku Hassan Bunza na Babbar Kotun Jihar Kebbi da wasu da ake zargin 'yan bindiga ne suka yi daga gidansa da ke Karamar Hukumar Bunza.

SHAHARARRIYAR 'YAR SIYASA MAI JINƘAN MARAYU TA YOBE, HAJIYA FATIMA UMAR MAIRIGA TA RASU

An shiga jimami a Jihar Yobe bayan rasuwar Hajiya Fatima Umar Mairiga, wadda ta kasance Mataimakiyar Shugabar Mata ta Jam'iyyar APC (Deputy Woman Leader)

Gwamna Buni Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitattun 'Ya'yan Yobe, Ya Bukaci A Yi Musu Addu'a

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Girma Hon. Mai Mala Buni, CON, COMN, ya bayyana alhininsa kan rasuwar wasu fitattun 'ya'yan jihar, tare da kira ga al'umma da su ci gaba da yi musu addu'ar samun rahama da kuma bai wa iyalansu goyon baya.

INEC Ta Fara Daukar Ma'aikatan Dindindin, Ta Bude Shafin Daukar Aiki Ga 'Yan Najeriya

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fara daukar sabbin ma'aikatan dindindin tare da bude shafin neman aikin ga 'yan Najeriya masu cancanta. Aikin ya shafi mukamai daban-daban na matakan Grade Level 8, 9, 10 da 12.

Ministan Ilimin Indiya Ya Yi Murabus Bayan Zanga-zangar Matasa Kan Satar Takardun Jarabawa

Ministan Ilimin Indiya, Dharmendra Pradhan, ya sanar da murabus dinsa a ranar Asabar, bayan kwanaki ana gudanar da zanga-zangar matasa a fadin kasar kan zargin satar da sayar da takardun jarabawar shiga manyan makarantun likitanci.

Gwamna Buni Ya Amince da Aiwatar da Yarjejeniyar FGN/ASUU ta 2025, Ya Ba da Umarnin Biyan Bashin Alawus ga Malaman Jami'a

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Girma Hon. Mai Mala Buni, CON, COMN, ya amince da aiwatar da yarjejeniyar shekarar 2025 da aka cimma tsakanin Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Malaman Jami'o'i (FGN/ASUU).

Gwamna Buni ya ja hankalin al’ummar masarautar Ngazargamu kan zaman lafiya da haɗin kai

Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni CON COMN, ya buƙaci al’ummar masarautar Ngazargamu da su haɗa kai tare da bai wa sabon Sarkin Ngazargamu, Alhaji Mahmud Ibn Mustapha, goyon baya domin samun nasarar mulkinsa mai amfani ga al’umma baki ɗaya.

Gwamnatin Jihar Yobe Ta Amince da Kashe Makudan Kuɗaɗe Kimanin Naira Biliyan 73.3 Domin Gudanar da Manyan Ayyuka

Majalisar Zartarwa ta Jihar Yobe (EXCO) ta amince da kashe kimanin Naira biliyan 73.3 domin aiwatar da manyan ayyukan ci gaba da kuma samar da ayyukan jin daɗin al'umma a faɗin jihar.

Jihar Jigawa Ta Kawo Karshen Rikicin Iyaka Tsakaninta da Jamhuriyar Nijar Bayan Shekaru 47

Gwamnatin Jihar Jigawa ta sanar da kawo ƙarshen rikicin iyaka da ya daɗe yana ci tsakanin al'ummar Jobi da ke Najeriya da kuma Kyalli da ke Jamhuriyar Nijar, rikicin da ya shafe kusan shekaru 47 yana ci tare da haddasa mutuwar sama da mutane 1,000.